21 Afirilu 2025 - 14:05
Source: ABNA24
Mutane 12 Ne Su Kai Shahada A Harin Da Jiragen Yaƙin Amurka Suka Kai A Yaman

Jiragen yakin Amurka sun tsananta hare-harensu a daren jiya da safiyar yau. Hare-haren sun kai su a garuruwa daban-daban a kasar Yaman sun yi sanadiyar mutuwar mutane akalla 12 tare da jikkata wasu 30 na daban.

Kamfanin dillancin labaran ƙasa da ƙasa na Ahl-Bait As -Abna- ya habarta bisa nakaltowa daga Al-Mayadeen cewa, a ci gaba da hare-haren wuce gona da irin da Amurka ke kaiwa kasar Yemen, jiragen yakin kasar sun kai wasu jerin hare-hare a wasu garuruwan kasar ta Yemen a safiyar yau litinin, lamarin da ya yi sanadiyar shahada da jikkata wasu fararen hula.

Wakilin Al-Mayadeen ya bayar da rahoton cewa, jiragen yakin Amurka sun sake kai hari a yankin Al-Juba da ke lardin Marib sau biyu a jere. Haka nan yankin Harf Sufyan da ke lardin Amran ya fuskanci hare-haren na Amurka har sau uku, sannan kuma an kai hari a yankin Jabal al-Mahurit da ke lardin al-Mahurit da ke yammacin Sanaa sau daya.

Kamfanin dillancin labaran Saba na kasar Yemen shima ya bayar da rahoton cewa, jiragen yakin Amurka sun kai hari a yankin Sirwah da ke lardin Marib har sau hudu.

An kuma bayar da rahoton hare-hare biyar da jiragen yakin Amurka suka kai a lardin Saada da ke arewacin kasar Yemen.

A cikin wadannan hare-haren, jiragen yaƙin na Amurka sun kai hari kan ababen more rayuwa na fararen hula na kasar Yemen, da suka hada da muhallan kiwon lafiya da tsafta a yankin Asr da babbar kasuwar jama'a da unguwar Faruah al-Shaabi da ke yankin Shu'ub, lamarin da ya janyo hasarar kudi ga gidaje da shaguna na 'yan kasar ta Yemen.

Ma'aikatar lafiya ta kasar Yemen a birnin San'a ta sanar da cewa, an kashe 'yan kasar Yemen 12, yayin da wasu 30 suka jikkata sakamakon harin da Amurka ta kai kan kasuwar Al-Farwa Al-Shaabi da unguwarsu, kuma da alama adadin ya karu.

Hare-haren da Amurka ke kaiwa kasar Yemen ya kara tsananta ne bayan da gwamnatin Isra'ila ta sake mamaye yankin Zirin Gaza tare da ci gaba da kai hare-hare a yankin. Dakarun kasar Yemen sun sake dawo da shingensu da hare-harensu na sojojin ruwa na gwamnatin kasar suka yi a tekun Bahar Maliya da kuma tekun Larabawa tare da kai farmaki kan jiragen ruwan Isra'ila domin nuna goyon bayan Gaza da kuma kare al'ummar Palastinu.

Your Comment

You are replying to: .
captcha