Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - Gabanin ranar tunawa da masallacin Quds ta duniya da ke tafe, Ayatullah Sayyid Ali Khamenei yayin wata ganawa da ya yi da kungiyar daliban jami'a da wakilan kungiyoyin dalibai jiya Talata a nan Tehran ya bayyana cewa "ranar Qudus ta bana za ta sha bamban da sauran da suka gabata.
Jagoran ya jinjinawa al'ummar Falastinu da ake zalunta, ya kuma ce Ranar Kudus wani lokaci ne da ya dace don nuna goyon baya ga al'ummar Palastinu da ake zalunta."
A daye bangaren kuma Jagoran ya soki soki yadda gwamnatin Sahayoniya take aikata munanan laifuka, kuma Amurka da Turai suna goyon bayansu”.
342/