6 Maris 2021 - 08:22
Najeriya:'Yan bindiga A Zamfara Sun Sace Mutane Fiye Da 60 A Garin Ruwan Tofa

Wasu kafafen yada labarai sun bayyana cewa ‘yan bindiga sun sace mutane fiye da 60 a garin Ruwan Tofa na karamar hukumar Maru a jihar Zamfara na tarayyar Najeriya a yau Alhamis.Labarin ya kara da cewa ‘yan bingidan sun kona fiye da rabin garin, sannan mutum guda ne yake jinya a asbiti.

ABNA24 : Wannan labarin ya na zuwa ne a dai-dai lokacinda gwamnatin tarayya take son kawo karshen satan mutane a arewacin kasar. Kafin haka dai ba’a dade da kwato wasu yan mata yan makarantar sakandari a jihar ba.

Kafin haka dai ‘yan bindigan sun sace wasu yan makaranta a jihar Katsina. Har’ila yau a wani labarin gwamnan jihar Zamfara ya bada sanarwa kafa dokar hana fita a garin Jangebe saboda kashe wutar zanga-zangar ta mutane garin dangane da ‘yan mata da aka sace a cikin yan kwanakin da suka gabata.

342/