“Ko ba komi kamin Manzon Allah (S) ya zo Madina, tuni ta karɓi musulunci, musulunci ya yaɗu a cikin Madina, saboda haka ko sadda ya zo, ba ya zo ba ne a matsayin ɗan gudun hijira ba, ya zo ne da sunan Shugaba, saboda baki ɗaya Madina maza da mata duk sun karɓi musulunci.
Ina muka kasance daga sakon wannan Annabi Mai Girma? Kuma ina al'umma ta kasance daga shirinta na Alkur'ani? Kuma ina matsayinta yake daga yaƙin gaskiya da ƙarya a lokacin da da yawa daga cikin 'ya'yanta suka yi watsi da asalinsu, suka ƙi ka'idojinsu, har ma karkata ta kai wasu zuwa matakin motsi a ƙarƙashin tutar azzalumi da girman kai na Amurka da Isra'ila, a daidai lokacin da ya kamata su kasance cikin addinin da ya ginu a kan adalci da daidaito da gaskiya.