5 Faburairu 2026 - 11:00
Source: ABNA24
An Kama Wanda Ake Zargi Da Hannu A Kisan Shahid Sayyid Hassan Nasrallah

Wani ɗan jarida ɗan ƙasar Lebanon ya sanar da cewa: Wani mutum da aka kama ka tsare a Cibiyar Tsaron Lebanon ya taka rawa wajen haɗin gwiwa da Isra'ila da tattara bayanai da suka kai ga kisan Sayyid Hassan Nasrallah.

Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (ABNA) ya habarta cewa: ɗan jaridar Lebanon "Abdullah Qamh" ya bayyana cewa ɗaya daga cikin mutanen da jami'an tsaron Lebanon suka tsare yana da hannu a shari'ar kisan gillar Sayyid Hassan Nasrallah, tsohon Sakataren Janar na Hizbullah.

Qamh ya ce a wata hira da aka yi da shi a talabijin: "Mutumin da Hukumar Tsaron Lebanon ta tsare, bisa ga binciken da aka gudanar, ya yi aiki kai tsaye da gwamnatin Sahyoniyawa kuma ba dan rundunar Hizbullah ba ne. Ya yi ikirari mai mahimmanci da haɗari. Daga cikinsu akwai cewa ya kan yi tafiya zuwa yankunan kudancin Beirut tare da wasu mutane kuma yana da ƙaramar na'ura a hannunsa kuma ya je wasu wurare waɗanda daga baya aka tabbatar da cewa bakin ramukan kasa ne na Hezbollah".

Ya ƙara da cewa: "Wannan na'urar tana da ikon tantance nisan da ke tsakanin ƙasa zuwa wuraren ƙarƙashin ƙasa, kuma wannan ya taimaka wa Isra'ilawa su tantance nau'in da ƙarfin bama-baman da suke buƙata don kai hare-hare ta sama da kuma kai hari kan waɗannan gine-ginen daidai".

Qamh ya ƙara jaddada cewa, bisa ga ikirarin wannan mutumin, ɗaya daga cikin yankunan da ya ziyarta shine yankin da Nasrallah ya yi shahada.

A cewar rahotanni, gwamnatin Sahyuniya ta kashe Sayyid Hassan Nasrallah a wani hari a ranar 27 ga Satumba, 2024 (6 Mehr 1403 AH). An gudanar da wannan aikin ne bayan da sojojin Isra'ila suka sami bayanai game da wani taro tsakanin kwamandojin Hizbullah a hedikwatar ƙungiyar da ke gefen kudancin Beirut.

A cewar majiyoyin da suka san lamarin, a cikin wannan aikin, jiragen yaƙi na gwamnatin Sahyoniya na F-35 sun jefa manyan bama-bamai masu ratsa jiki waɗanda suka kai sama da fam dubu biyu a kan wuraren da aka keɓe, wanda ya haifar da lalata gine-gine shida gaba ɗaya da kuma kai hari kan hedikwatar Hizbullah.

Your Comment

You are replying to: .
captcha