7 Disamba 2025 - 07:54
Source: ABNA24
Yamen: Mamayar Da Saudiyya Da Hadaddiyar Daular Larabawa Suke Yi Wa Gabashin Yemen Zai Kawo Karshe.

Ansarullah tayi gargadi ga yan barandan kasashen Saudiyya da Daular Larabawa game da mamaye wasu yankunan kasar

Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na na Ahlul Baiti (AS) – ABNA– ya habarto cewa: Sanaa, tana mai jaddada matsayinta kai tsaye ta sanar da cewa motsin da Saudiyya da Hadaddiyar Daular Larabawa suka yi kwanan nan a gabashin Yemen, musamman a Hadramaut da Al-Mahra, yana nuna ƙoƙarin ƙasashen biyu na ƙarfafa mamayar yankuna masu muhimmanci a Yemen; amma ƙarshen wannan mamayar tasu ya kusa zuwa.

A cewar jami'an Yemen, babu wata rundunar ƙasashen waje da ke da ikon tsoma baki a cikin ikon mallakar ƙasar Yemen, kuma gwagwarmayar jama'a tare da dabarun Ansarullah na dogon lokaci za su zama babban abin da zai canza daidaiton ƙasar nan gaba.

Your Comment

You are replying to: .
captcha