Kamfanin dillancin labaran ƙasa da ƙasa na Ahlulbayt (AS) - ABNA - ya habarta cewa: Wani wurin na daban kuma da ke da alaƙa da naúrar 8200 shima an kai masa harin. A cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Talata, dakarun kare juyin juya halin Musulunci (IRGC) sun tabbatar da nasarar hare-haren da aka yi kan sashin leken asirin sojin Isra'ila mai lamba 8200 a sansanin Glilot da ke kusa da Tel Aviv.
"Da sanyin safiyar yau Talata, 17 ga watan Yuni, IRGC Aerospace Division, a cikin wani aiki mai nasara da tasiri, duk da kasancewar tsarin tsaro masu ci gaba sosai, sun afkawa cibiyar leken asirin soja ta sahyoniyawa da aka fi sani da Aman da Cibiyar Tsare-tsaren ta'addanci da munanan tsarin mulkin sahyoniyawa na (Mossad) a Tel Aviv, kuma a halin yanzu wannan cibiya tana cin wuta.
Hotunan da ke yawo a shafukan sada zumunta a ranar Talata sun nuna cibiyar dabaru ta 'Aman', wani bangare na rukunin leken asirin sojan Isra'ila da ke Glilot kusa da Tel Aviv, tana ci da wuta. An san Aman a matsayin ɗaya daga cikin tsoffin ƙungiyoyin leƙen asiri da aka kafa jim kaɗan bayan da kafa haramtacciyar kasar Isra'ila. Babban manufarta ita ce ta tattara tare da ba da bayanan sirri ga gwamnatin Isra'ila da hukumar leken asiri, Mossad, saboda ta'addanci da zagon kasa a fadin duniya, ciki har da Iran.
Aman ta haɗa da rukunin leƙen asiri na fasaha na tsaro waɗanda ke ba da damar hare-haren soja na musamman kamar Unit 8200 (Signals Intelligence), Unit 504 (Human Intelligence), da Unit 9900 (Geospatial Intelligence). Duk da haramcin buga hotunan da ke da alaka da asarar da gwamnatin ta yi a ci gaba da gudanar aikin Alkawarin Gaskiya III, wanda Dakarun kare juyin juya halin Musulunci (IRGC) ta gudanar, an fitar da faifan bidiyo da yawa da ke nuna cibiyar Aman ta cikin babbakewa da wuta. An kai harin ne da sanyin safiyar Talata, a kashi na tara na aikin Alkawarin Gaskiya wanda ya fara a daren Juma'a bayan da gwamnatin Isra'ila ta kashe wasu manyan kwamandojin sojin Iran, masana kimiyyar nukiliya da fararen hula, ciki har da mata da yara. Tun a ranar Juma'a, gwamnatin Isra'ila ta ke ci gaba da cin zarafi ga Jamhuriyar Musulunci ta Iran, tana kai jerin hare-hare kan fararen hula. A ranar Litinin, ta kai hari kan ginin gidan redio Jamhuriyar Musulunci ta Iran (IRIB) a Tehran yayin watsa labaran kai tsaye, wanda ya yi sanadiyar shahadar 'yan jarida biyu. Iran ta yi kira ga kasashen duniya da su yi Allah wadai da kuma dora wa gwamnatin Israila alhakin ci gaba da cin zarafin kasar, yayin da ta sha alwashin kare kasarta da dukkan hanyoyin da take da su. Birgediya Janar Ahmad Wahidi, babban mai ba da shawara ga kwamandan IRGC, a cikin jawabinsa a ranar Litinin ya ce sabbin makamai masu linzami na Iran suna wakiltar wani kaso ne kawai na ci gaban sojin kasar. "Za mu tura kayan aikin mu masu ci gaba a duk lokacin da ake ganin ya cancanta. Tunanin cewa tarin makamin mu yana raguwa abin dariya ne. Har yanzu ba mu yi amfani da dabarun mu ba, ”in ji shi.
Your Comment