15 Agusta 2024 - 07:05
Malaman Yahudawa 100 Sun Rubuta Wasika Zuwa Ga Netanyahu Don Ya Amince Da Yarjejeniyar Tsagaita Wuta

Wannan wasiƙar ta ce: "Karbar yarjejeniya abu ne da ya shafi Yahudawa da ɗabi'a wanda ya kamata a gudanar da shi yanzu".

Kamfanin dillancin labaran kasa da kasa na Ahlul-Bait (a.s) ya habarta maku cewa: Tashar yada labarai ta Kan Isra’ila ya bayar da rahoton cewa, sama da malaman addinin yahudawan Amurka 100 ne suka rubuta wasika ga Benjamin Netanyahu, inda suka bukaci ya amince da yarjejeniyar tsagaita bude wuta da kuma musayar fursunoni.

A cewar sanarwar cibiyar sadarwa ta "Kan", wannan wasiƙar ta ce: "Karbar yarjejeniya abu ne da ya shafi Yahudawa da ɗabi'a wanda ya kamata a gudanar da shi yanzu".