Sojojin Najeriya sun sanar da kubutar da mutane 45 da aka yi garkuwa da su a yayin ayyukan tsaro daban-daban da aka gudanar a jihohin Edo da Borno, tare da kama wasu da ake zargi da haɗin kai da ƙungiyar "ISIS" da kuma wargaza wata ƙungiyar ta’addanci a jihohin Delta da Rivers.
A daidai lokacin da ake gudanar da jana'izar gawar jagora shahidin juyin juya halin Musulunci da iyalinsa a Iran da Iraki, wasu gungun mambobin Harkar Musulunci ta Najeriya karkashin jagorancin Sheikh Ibrahim Zakzaky, sun gudanar da jana'izar alamci da rakiyar shugaba mai girma na Musulunci a jihar Bauchi, Najeriya.