11 Ga Watan Zul-Ka'adah A irin wannan rana ce a Shekara ta 148 bayan hijirah aka haifi Imamu Ali Ar-Ridha (as) a Garin Madinah, wato a Shekarar da Kakansa Imamu Sadiq (as) ya yi Shahada. Shi ne Imami na 8 daga jerin Limaman Shiriya 12 da Ma'aiki (Saww) ya ce Mu yi riko da Su a bayansa.
Na farko, fikihu amsoshin addini ne ga bukatu a aikace na dai-dai kun mutane da al'umma. Tare da haɓakar kaifin hankali na canjawar tsatso, wannan bukatun dole ne, a yau fiye da kowane lokaci, su kasance suna da tushe mai tushe na hankali da na ilimi, kuma su zamo wadaanda za’a iya fahimta da ganewa.