Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (AS) – ABNA - ya habarta cewa: Kwamandan dakarun "Golani" na sojojin Sahayoniya ya mutu sakamakon harin wani jirgin marasa matuki na Hizbullah a yankin Deir Siryan da ke kudancin Lebanon; a lokaci guda kuma ayyukan Hizbullah na ci gaba da mayar da martani ga hare-haren Isra’ila.
Kakakin sojojin Sahayoniya a yau Asabar ya bayyana cewa wani Kaftin kuma kwamandan tawaga a bataliya ta 12 na Rundunar Golani ya mutu sakamakon fashewar wani jirgin marasa matuki na kunar bakin wake a kusa da kogin Litani a kudancin Lebanon.
Dangane da haka, kafofin yada labaran Isra'ila sun ruwaito cewa jiya Juma'a da misalin karfe biyu na rana, Hizbullah ta harba wani jirgin marasa matuki na kunar bakin wake zuwa ga wani rukunin sojoji na bataliya ta 12 na Golani da ke aiki a ƙauyen Deir Siryan kusa da yankin Taybeh a kudancin Lebanon. Wannan jirgin marasa matuki ya afkawa sojojin, sakamakon haka wannan Kaftin ya mutu kuma wani soja ya ji rauni.
Haka kuma, a cewar waɗannan kafofin yada labarai, Hizbullah ta harba jiragen marasa matuki na kunar bakin wake tare da harba manyan harsasai na zuwa ga waɗannan sojojin; sojojin da a zahiri suka shafe sa'o'i suna fuskantar barin wuta.
Waɗannan kafofin yada labarai sun kara da cewa wannan lamari ya faru ne kwana ɗaya bayan da Hizbullah ta kai hari kan wuraren wannan rundunar ta bataliyar Golani a wannan ƙauyen manyan bindigu; harin da wani sojan Isra'ila ya mutu a cikinsa.
Majiyoyin Isra'ila sun kuma yi nuni da cewa sojojin Sahayoniya sun makale a cikin cakwalkwalin Lebanon, in da suka ce yawan fitar da sanarwar kashewa da raunata sojojin a kullum da ci gaba da harbi a arewacin yankunan da aka mamaye, yanayi ne da ba zai iya ci gaba ba.
Hizbullah jiya Juma'a ta bayyana cewa ta kai hari kan taron sojojin a kewayen kogin Deir Siryan a kudancin Lebanon da wani jirgin marasa matuki na kunar bakin wake. Wannan aiki yana daga cikin ayyuka 33 da Hizbullah ta bayyana jiya Juma'a, wanda shine mafi yawan ayyukan wannan ƙungiyar tun lokacin da aka fara tsagaita wuta ta wucin gadi tsakanin Lebanon da Isra’ila a ranar 17 ga Afrilu da ta gabata.
A yau Asabar ma, Hizbullah ta ba da labarin aiwatar da wasu ayyuka 11 da suka haɗa da kai hari mai yawa na bindigogi a dukan wuraren sojojin Isra'ila a yankin al-Bayada tare da manyan bindigogi da ruwan harsasai na rokoki.
A wani bangaren kuma, Sojojin Sahayoniya na ci gaba da kai hare-haren sama musamman a kan ƙauyukan kudancin Lebanon; hare-haren da suka kai ga shahada da raunata wasu 'yan ƙasar Lebanon, kuma bisa alkaluman da aka bayyana, adadin shahidai da wadanda suka ji rauni a hare-haren Isra’ila a Lebanon daga ranar 2 ga Maris zuwa yanzu ya kai shahidai 2,969 da raunata 9,112.
Your Comment