9 Agusta 2025 - 14:17
Source: ABNA24
Manyan Jami'an Leken Isra'ila Na Adawa Da Batun Mamayar Gaza

Kafofin yada labaran Sahayoniya: Mossad da Shin Bet suna adawa da shirin mamayar Gaza

Kamfanin Dillancin Labarain ƙasa da ƙasa Ahlul-Baiti (ABNA) ya ruwaito cewa: Jaridar yahudawan sahyoniya ta Yedioth Ahronoth ta bayyana cewa shugabannin hukumar leken asiri ta gwamnatin Mossad da hukumar tsaron cikin gidanta Shin Bet sun nuna adawa da shirin mamaye birnin Gaza sakamakon tsoronsu da sakamakon hakan zai haifar.

Dangane da haka ne gidan talabijin na Sahayoniyya Channel 12 ya ruwaito cewa Tzachi Hangbi shugaban kwamitin tsaron Isra'ila ya nuna adawa da shirin Netanyahu na Gaza a wani taron majalisar ministocin kasar da aka gabatar.

Your Comment

You are replying to: .
captcha