8 Afirilu 2022 - 20:18
Kasar Ruwanda Na Bikin Tunawa Da Cika shekaru 28 Da Kisan Gilla Da Akayi Wa Yan Tutsi

Shekaru 28 ke nan da suka gabata da kawo karshen yakin basasa da aka yi a aksar Rwanci, day a haddasa rasa rayukan mutane sama da 800,000 yan kabilar Tutsi da kuma masu saussaucin ra’ayi a kabilar Hutu,a cikin kwanaki 100.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - A Bana kungiyar tarayyar Afrika ta zabi taken wannan shekarar a matsayin shekarar tunawa da hadinkai da kuma sabuntawa da Jaddada aniyar da ake da shi na daukar tsauraren mataken hana sake afkuwar yakin kare dangin a nahiayr baki daya

A ranar 7 ga watan Aprilu ne shugaban kasar Ruanda Paul Kagame ya data fitala a birnin Kagali domin tunawa da kisan kare dangi da aka yi a kasar, inda sama da mutane 250.000 lamarin ya shafa, kuma za’a ci gaba da gudanar da bikin juyayin har zuwa ranar 13 ga watan Aprilu. Kuma za’a kwashe kawano 100 a na gudanar da tarurruka na tsawo kwanakin da aka kwashe ana tafka kisan kiyashin

A shekara ta 2021 ne shugaban kasar Faransa Emanual Makron ya ce kasar faransa ta taka rawa , amma bai ce a bangaren kisan kiyashin ba, shi ne shugaban kasa ko wani babban jami’I a na farko da ya taba furta hakan, inda aka ganinsa a matsayin daya daga cikin kisan kiyashi da aka yi mafi muni a zamanin nan.

342/