Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - Kakakin gwamnatin sojan kasar ta Mali KAnar Abdullahi Maiga ya nemi ganin minister tsaron Faransa Florence Parly da ta daina Magana akan kasar ta Mali.
Maiga wanda ya bayyana hakan a wata hira ta kafar Talbijin ya yi watsi da zargin da ministar ta Faransa ta yi wa kasarsa da tsonaka a yankin Sahel.
Tun a cikin watan Ogusta na 2020 e da sojoji su ka kifar da gwamnatin Bubakar Keita, alaka a tsakanin Faransa da Malin ta yi kamari.
Mali da bukaci ganin sojojin Danmark da suke aiki a ciki kasar ta Mali da su fice, lamarin da haddasa sabani a tsakaninta da Faransa. Sojojin na Danmark da sun shiga cikin kasar Mali ne domin su taimakawa na kasar Faransa a karkashin farmakin da suke kira da Takuba.
342/