Kwamitin Tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya a wani taro ya nuna damuwa game da rikice-rikicen da ke ƙaruwa a Afirka ta Tsakiya ciki har da yaƙi a Sudan, barazanar ƙungiyar ta'adda ta Boko Haram, gudun hijira mai yawa da kuma yaɗuwar cutar Ebola. "Martha Ama Akyaa Pobee" wakiliyar Majalisar Ɗinkin Duniya a wannan taro ta yi gargadin cewa martanin soji kaɗai ba zai magance waɗannan rikice-rikicen ba, kuma gudun hijira, ta'addanci, matsin tattalin arziki da takaita 'yancin jama'a suna matsawa kasashe da yawa a yankin lokaci guda.