A matakin farko na martani na ladabtarwa ga masu karya alkawari Amurka, mayakan sojojin ruwa da sararin samaniya na dakarun juyin musulunci, bayan sa'a guda daga hare-haren da suka kai wa yankuna daban-daban na ƙasar, a wani aiki na hadin gwiwa da makamai masu linzami da jirage mara matuki, sun kai hari mai barna a kan ababen more rayuwa da muhimman cibiyoyi na sansanonin mulkin mallaka na Amurka guda biyu, wato: "Arifjan" da "Ali Al-Salem" a Kuwait, da sansanonin "Jufair" da "Sheikh Isa" a Bahrain.