Ƙungiyar Gwagwarmayar Musulunci ta Hamas a yau (Laraba) ta ɗorawa gwamnatin Sahayoniya alhakin rugujewar ginin Al-Sa'adah a kan mazauna da 'yan gudun hijira a birnin Gaza kuma ta kwatanta wannan lamari a matsayin sabon babi na musiba ga ɗan adam mai ban tsoro na yaƙin kisan kare dangi kan Zirin Gaza. Tun da sanyin safiyar yau, ƙungiyoyin agaji na Falasɗinawa sun ciro gawar shahidai 20 ciki har da yara 6 daga ƙarƙashin baraguzai kuma wasu da dama har yanzu ba a same su ba.