Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : ABNA24
Jummaʼa

28 Oktoba 2022

18:15:05
1318085

Sayyid Hassan Nasrallah: ISIS Har yanzu Tana Gudanar Da Ayyukan Amurka A Afghanistan.

Masu Shirya Hargitsi A Iran Su Ne Masu Aikata Laifukan Ta'addanci A Shiraz

Babban sakataren kungiyar Hizbullah ya yi jawabi ga al'ummar Iran inda ya ce: Ku tabbata cewa masu tayar da tarzoma a Iran su ne suka tura 'yan ta'adda zuwa Shiraz waɗannan ayyuka biyun Suna karakashin gudanarwa guda ɗaya da baƙar tushe guda ɗaya wanda "Amurka" ke gudanarwa.

Kamfanin dillancin labaran Ahlul-Bait (AS) - ABNA -ya kawo maku rahotan cewa: “Syed Hassan Nasrallah” babban sakataren kungiyar Hizbullah ta kasar Labanon ya gabatar da jawabi a yayin bude kasuwar noma ta cikin gida da aka baje kolin kayayyakin abinci da na ayyukan hannu", wanda kungiyar Jihad Gine-gine ta kasar Lebanon ta shirya.

A farkon jawabin nasa ya bayyana ta'aziyyarsa ga Jagoran juyin juya halin Musulunci, jami'an Iran, al'ummar Iran da iyalan shahidai, ya kuma yi addu'ar samun rahama ga shahidan da kuma waraka ga wadanda suka jikkata.

Sayyid Hasan Nasrallah ya kara da cewa: Batu na farko shi ne mumunan kisan kiyashi da kungiyar ISIS ta yi a birnin Shiraz na kasar Iran. Wannan danyen aikin ya kamata ya kara wayar da kan al'ummomin wannan yanki musamman al'ummar Iran da ke fuskantar wata makarkashiya mai hadari ta Gwamnatocin Amurka da suka gada sun hada kan kungiyar ISIS da sauran kungiyoyin takfiriyya tare da samar da sharudda wajen zama ga shugabanni da wasu bangarorin wadannan kungiyoyin a Afganistan cikin aminci.

Babban sakataren kungiyar Hizbullah ya yi jawabi ga al'ummar Iran inda ya ce: Ku tabbata cewa masu tayar da tarzoma a Iran su ne suka tura 'yan ta'adda zuwa Shiraz waɗannan ayyuka biyun Suna karakashin gudanarwa guda ɗaya da baƙar tushe guda ɗaya wanda "Amurka" ke gudanarwa.

Bayan kammala ayyukanta a Siriya da Iraki, yanzu ISIS tana da manufa ta Amurka don aiwatar da wani shirinta a sabon wurinta - da ke Afghanistan.

Ya ci gaba da cewa: Dole ne mu kara wayar da kan jama'a da fahimtar muhimmancin jihadi mai girma da da dama a yankinmu suke yi Jamhuriyar Musulunci ta Iran ita ce mafi karfin goyon bayan wannan jihadi mai girma, wanda kwamandojinta suka kasance shahidai Suleimani da Al-Muhandis .

Sayyid Hasan Nasrallah ya kuma ci gaba da ishara da irin gwagwarmayar da al'ummar Palastinu suke yi inda ya ce: Gaisuwa ga jajirtattun mayaka masu gwagwarmaya a Kudus da Yammacin Gabar Kogin Jordan - musamman a Nablus, Jenin da Shufat - da kuma gaisuwa ga shahidi "Udi al. Tamimi" wanda ya zama alami ga tsatso masu tasowa wanda za su samu cin nasara.

Ya kara da cewa: Gaisuwa ga jaruman kungiyar Erin Al-Asud (Bisheh Shiran) da Jenin Battalion. Wadannan jaruman sun girgiza makiya tsawon makonni. Ana dai fatan wannan yunkuri zai sauya daidaito da kuma samar da fagen samun nasarar karshe ta al'ummar Palasdinu.

Babban sakataren kungiyar Hizbullah ta kasar Labanon ya yi ishara da cewa: Jaruman Palastinawa da mayaka a yammacin gabar kogin Jordan sun shafe makwanni suna kai munanan hare-hare ga gwamnatin sahyoniyawa, kuma duk da cewa adadinsu ba su da yawa, kuma albarkatunsu kadan ne, amma ruhinsu na da yawa. Abin da ke faruwa a Yammacin Kogin Jordan yana tsara sabon hanya a Falasdinu don samun 'yanci mai girma.

Sayyid Hasan Nasrallah ya kuma bayyana dangane da yarjejeniyar zana iyakar tekun kasar Labanon cewa: Zane iyakar teku lamari ne da ya cancanci a yi bayani dalla-dalla, don haka za mu yi magana dalla-dalla a ranar Asabar. Dangane da batun kayyade iyakokin ruwa da gwamnatin sahyoniyawan, abin da ya faru tun daga farko har karshe wata babbar nasara ce ga kasar Labanon; Ga gwamnati, ga jama'a da Gwagwarmaya. A yau, Lebanon ta wuce wani muhimmin mataki da ya sanya ta cikin wani sabon yanayi.

Ya ci gaba da cewa: "Aikin Gwagwarmaya a shari'ar raba kan iyaka ya kare, kuma a yau ina sanar da cewa an kammala dukkan matakan da matakan da aka dauka a baya." Ina gode wa mayaƙan da suka yi aiki dare da rana kuma sun ce aikin ya ƙare. Abin da aka cimma a shari'ar raba kan iyakokin wata babbar nasara ce ga gwamnati da al'ummar kasar da kuma gwagwarmayar Lebanon.

Sayyid Hasan Nasrallah a martanin da ya yi kan batun rattaba hannu kan yarjejeniyar shata iyakokin tekun Labanon da Isra'ila, shin wannan yana nufin ginshikin daidaita alaka da gwamnatin yahudawan sahyoniya ne?. sai yake cewa: Dukkan shawarwarin da ake yi dangane da batun kan iyakokin tekun a kaikaice ne ba kai tsaye ba ne kuma tawagogin Lebanon da yahudawan sahyoniya ba su taba haduwa a wuri guda daya ba, ba su hadu da juna ba. Abin da shugaban kasar ya sanya wa hannu kuma za a sanar da shi a birnin "Al Naqura" ba yarjejeniyar kasa da kasa ba ce kuma bai hada da daidaita alaka da Isra'ila ba.

Babban sakataren kungiyar Hizbullah ta kasar Labanon ya sanar da cewa: Jami'an kasar Lebanon sun yi taka tsantsan wajen daukar wani mataki da zai haifar da shakku kan hakan. Duk wani magana game da daidaitawa ba shi da tushe. Makiya yahudawan sahyoniya sun yarda cewa, ba a cimma wani garantin tsaro ba dangane da zana iyakar teku.

Haka nan kuma ya yi tsokaci kan yadda kungiyar Hizbullah ke taka rawa wajen yaki da cutar kwalara inda ya ce: Hizbullah ta hada kai da ma'aikatar lafiya ta kasar Lebanon wajen yaki da cutar kwalara.

Babban sakataren kungiyar Hizbullah ta kasar Labanon ya ci gaba da cewa: Al'ummar kasar Labanon ba za su jira ba, idan da a ce Gwagwarmaya bata jira gwamnati ba tun a shekarar 1982, da har yanzu muna karkashin mamayar Isra'ila, kuma ba za a yi amfani da batun 23 ba.

Ya kara da cewa: Kada mu manta cewa, duk da mawuyacin halin da kasar Siriya ta shiga, hadin gwiwar cibiyar gine-gine ta Jihad da ma'aikatar aikin gona ta kasar Siriya ba ta tsaya tsayin daka ba tsawon shekaru da suka gabata. Jihadin gine-gine yana kan gaba da cigaba a halin yanzu.