17 Mayu 2026 - 02:16
Source: ABNA24
Saƙon Sana'a Ga Khalil Hayya: Muna Tare Da Al'ummar Falasdinu

Mataimakin ministan harkokin wajen Yemen, ta hanyar aika saƙo zuwa ga Khalil Hayya, shugaban ofishin siyasar Hamas a Gaza, ya yi ta'aziyya kan shahadar kwamandan rundunar Ezziddin Qassam.

Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (ABNA) ya habarta cewa: A cikin wannan saƙo yazo cewa: Muna mika ta'aziyyarmu mafi zurfi da tsattaar juyayinmu ga Dokta Hayya, da iyalin shahidi Abu Suhaib (Ezziddin Haddad), da al'ummar Falasdinu.

Laifukan ta'addancin matsorata na makiya ba za su hana al'ummar Falasdinu gwagwarmaya da juriyarsu ba game da fuskantar mamayar Isra'ila.

Jinin shahidai zai kara karfafa juriyar Falasdinu don ta samu nasarar da aka yi alkawari ta hanyar tsayawa, juriya da kaiwa ga manufofinta.

Jamhuriyar Yemen tana goyon bayan al'ummar Falasdinu da juriyarsu har zuwa kawo karshen mamayar sahayoniyawa.

.......

Tags

Your Comment

You are replying to: .
captcha