16 Afirilu 2026 - 23:51
Source: ABNA24
Hizbullahi Ta Yi Ruwan Makamai Akan Arewacin Isra'ila + Bidiyoyi

Kungiyar Hizbullah ta harba manyan makamai masu linzami a yankunan arewacin Isra'ila tare da aukuwar fashe-fashe.

Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (ABNA) ya habarta cewa: Kafofin yada labarai na Hebrew sun ba da rahoton cewa, an samu fashe-fashe a ciki da kewayen yankin Naharia da aka mamaye bayan harba makamai masu linzami na kungiyar Hizbullah.

Hukumar ba da agajin gaggawa ta Isra'ila (Star of David) ta sanar da cewa mutane da dama sun samu munanan raunuka sakamakon harin makami mai linzami na kungiyar Hizbullah a birnin Karmel. An ba da rahoton fashe-fashe da dama a birnin Karmiel sakamakon harba makamai masu linzami da kungiyar Hizbullah ta yi. Haka kuma an samu rahotannin mutuwar wani dan kasar Isra'ila. Jami'an tsaron Isra'ila na kokarin jigila da kwashe wadanda suka jikkata da waɗanda suka mutu a hare-haren.

Kafofin yada labaran Isra'ila sun ba da rahoton cewa, kungiyar Hizbullah ta harba makamai masu linzami 20 a garuruwan Karmil da Naharia cikin 'yan mintoci kadan.

Your Comment

You are replying to: .
captcha