27 Faburairu 2026 - 23:47
Source: ABNA24
Taliban Ta Dauki Alhakin Hare-Haren Sama Da Aka Kai Wa Sansanonin Soji A Pakistan.

Ma'aikatar Tsaro ta Afghanistan ta sanar da cewa Taliban ta kai hare-haren sama kan sansanonin soji na Pakistan da ke Islamabad, tana mai cewa suna daukar fansa ne kan hare-haren da Pakistan ta kai a baya a Kabul, Kandahar, da Paktia. Pakistan ba ta fitar da wata sanarwa a hukumance ba tukuna.

Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (ABNA) ya ruwaito cewa: Ma'aikatar Tsaron Afghanistan ta sanar da cewa sojojin saman Taliban sun kai hare-hare kan sansanonin soji da dama a Islamabad a matsayin martani ga hare-haren sama da Pakistan ta kai wa Kabul, Kandahar, da Paktia a daren jiya.

Ma'aikatar Tsaron Afghanistan Ta Bayyana Cewa Aikin Ya Yi Nasara Sosai.

Rahotannin sun kuma nuna yiwuwar kai hari ta jirgin sama mara matuki kan makarantar soji ta Pakistan da ke Kakul, kodayake babu wani martani a hukumance daga Pakistan.

Mai magana da yawun Taliban Zabihullah Mujahid ya tabbatar da cewa Afghanistan har yanzu tana son yin tattaunawar zaman lafiya da Pakistan, amma Pakistan ba ta nuna shirin magance matsalolin ta hanyar tattaunawa ba.

Wannan yanayi da ake ciki a yanzu yana nuna karuwar tashe-tashen hankula tsakanin Taliban da Pakistan, inda bangarorin biyu ke ambaton hare-haren ketare iyaka da kuma goyon bayan kungiyoyin 'yan bindiga, lamarin da ya sanya makomar dangantaka tsakanin Kabul da Islamabad cikin rashin tabbas.

Your Comment

You are replying to: .
captcha