-
Rahoto Kan Hare-Haren Da Gwamnatin Mamaya Ta Kai A Yankuna Daban-Daban Na Gaza Cikin Sa'o'i Kadan Da Suka Gabata
Dakarun mamaya sun kai hari a yankunan arewacin birnin Gaza, kuma a lokacin da aka kai hare-hare ta sama a yankin Al-Tuffah da ke gabashin birnin Gaza, Falasdinawa biyu sun yi shahada tare da jikkata wasu da dama.
-
Fashewar Tashar Jiragen Ruwan Shahid Rajaee Ta Yi Sanadiyyar Mutuwa Da Bacewar Da Dama, Da Jikkatar Sama Da 700
Wani babban fashewa da ya auku a yau, Asabar 26 ga watan Aprilu 2025, a tashar jirgin ruwa ta Shahid Rajaee da ke Bandar Abbas, ya yi sanadin mutuwar mutane da dama da bacewar wasu da har yanzu ba iya sanin adadinsu ba tare da jikkatar 700, amma babu cikakken bayani kan musabbabin lamarin.
-
Ana Ci Gaba Da Gudanar Da Jarrabawar Mako-Mako A Jami’atul Mustafa (S) Science College, Darus-Salaam - Tanzania + Hotuna
Kamfanin dillancin labaran kasa da kasa na Ahlul Bayt As – ABNA - ya habarta cewa: Daliban Jami'atu Al-Mustafa (s) na ci gaba da gudanar da jarrabawarsu na mako-mako. Ana gudanar da wadannan jarrabawa ne duk ranar Asabar a wannan Kwalejin. Jarabawa ne masu mahimmanci waɗanda ke taimaka wa ɗalibai haɓaka karatunsu da ƙara mai da hankali kan abin da ake koya musu a cikin aji. Wannan matakin yana gina ɗalibi kuma yana ƙarfafa su a fannin ilimi, a ƙarshe su zama ƙwararrun ɗalibai wadanda suka sami nasara a karatunsu.
-
Dubban 'Yan Ƙasar Yemen Ne Suka Gudanar Da Zanga-Zanga A Faɗin Ƙasar Domin Yin Allah Wadai Da Ta'addancin Amurka Da Isra'ila
Al'ummar kasar Yemen sun sake gudanar da jerin gwano a fadin kasar, inda suke jaddada goyon bayansu ga Falasdinawa yayin da suke yin Allah wadai da hare-haren da Amurka ke kaiwa kasarsu.
-
Abubuwa Sun Fashe A Tashar Ruwan Bandar Abbas
A cewar wasu kafofin yada labarai: Ba tankin ammonia ne ya haddasa fashewar ba. Fashewar wani kwantena ne, amma har yanzu ba a san abin da ke cikin kwantenan ba.