Malamin yayi bayani da dama akan waki'ar data faru a 12-14 ga disambar shekara ta 2015 inda jimi’an tsaro tsawon wadannan raneku suka farwa mabiya Ahlul Bayt da kisa ba ji ba gani inda suka kai hari Husainiyah Baqiyatullah inda Shekh din ke gudanar da karatutta da kuma gidan sa dake unguwar Gyallesu cikin birnin Zaria da kuma Makabarta ta Darur Rahama inda suka kashe kowa a Husainiyya tare da rusheta sannan gidan Shekh din ma sun kashe kowa sannan suka kama malamin tare da mai dakinsa suka tafi dasu bayan sun harbe su harbi na kisa. Inda suka tsare sun a tsawon shekuru shida ba tare da laifin komai ba ko wani dalili.
Malamin ya ci gaba da bayani inda Yace dangane da Shekh Zakzaky : Matukar Addinin Musulunci Yana Raye To Lalle Shekh Zakzaky Yana Raye
Inda kuma ya kwatanta Malama Zenatudden Ibrahim da cewa: har yanzu Masu Kama Da Sayyidah Ummul Baniin Basu Kare Ba Malama Ta Kasance Ummul Banin Din Zamanin Mu...
Akarshe Anyi Addua ga daukacin wadanda sukai Shahada da nema masu rahamar Allah Ta'ala ga kuma wadanda suka wanzu da samun sabati da kariya daga makiya.
Rahoto: Shafiu Kabiru