Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (ABNA) ya bayar da rahoton cewa: Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci a Iran, Ayatullah Sayyid Ali Khamenei, ya tabbatar da cewa "al'ummar Iran za su mayar da martani mai ƙarfi ga duk wani hari da aka kai musu," yana mai jaddada cewa "Iran ba ta neman yaƙi ba kuma ba ta fara shi ba, amma duk wani hari da aka kai mata za ta mayar da martani mai ƙarfi kuma zai iya haifar da yaƙin yanki".
A lokacin ganawarsa da taron 'yan ƙasa a Husainiyyar Imam Khomeini (RA), Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya bayyana cewa "barazanar da Amurka ta ke ta maimaitawa, ta hanyar maganar tara rundunar sojoji ko zaɓuɓɓukan da ke kan teburi, ba sabon abu ba ne kuma ba za ta shafi ra'ayin mutanen Iran ba," ya ƙara da cewa "ƙoƙarin tsoratar da Iraniyawa ya gaza a baya kuma ba zai yi nasara a yau ba".
Ya yi nuni da cewa ƙasarsa ba ta kai wa kowace ƙasa hari ba, amma ba za ta yi jinkiri da kasa agwiwa ba wajen kare kanta, yana mai gargaɗin cewa "Kunna kowa ne irin yaƙi a wannan karon ba zai iyakantacce ba".
A wani yanayi makamancin haka, Imam Khamenei ya yi ishara da cewa "tashin hankalin da ya faru kwanan nan a ƙasar ya yi kama da wani yunƙurin juyin mulki, wanda aka yi niyya don kai hari kan cibiyoyin gwamnati masu mahimmanci, ta hanyar kai hari ga jami'an tsaro, cibiyoyin gwamnati da muhimman kayayyakin more rayuwa, yana mai jaddada cewa an dakile wannan yunƙurin".
Your Comment