Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : Islamic Movement
Talata

6 Agusta 2019

07:33:09
967313

Jawabin Sayyida Suhaila game da maganar dakatar da muzaharori

Daya daga cikin ‘ya’yan jagoran Harkar Musulunci a Nigeria Sayyid Ibrahim Zakzaky watau Sayyida Suhaila Ibrahim ta fitar da wani gajeren jawabi na Bidiyo inda take bayyana cewa batun kira da dakatar da muzaharori na bayan ba shi da wani asasi, kuma ba ra’ayin mahaifin ta bane.

(ABNA24.com) Daya daga cikin ‘ya’yan jagoran Harkar Musulunci a Nigeria Sayyid Ibrahim Zakzaky watau Sayyida Suhaila Ibrahim ta fitar da wani gajeren jawabi na Bidiyo inda take bayyana cewa batun kira da dakatar da muzaharori na bayan ba shi da wani asasi, kuma ba ra’ayin mahaifin ta bane.

Sayyida Suhaila ta bayyana cewa wanda ya bayyana haka shugaban bangaren yada labarai ne kuma Editan jaridar Almizan, amma ba yana magana da yawun Harkar musulunci bane, kuma ma babu wannan abin a cikin Harka.

Kamar dai yadda aka sani ne shi Sayyid Ibrahim Zakzaky ya sha nanata cewa mu ba kungiya bane Motsi ne, kuma dukkanin ibadojin mu da kusancin mu ga Allah yana cikin wannan motsin namu.

Sallolin mu, azumin mu, Hajjin mu, Zakkar mu, gwagwarmayar, mahangar mu, da dai sauran su, shine wannan motsin.



/129