Rahotannin sun ce tun jiya ne dai miliyoyin mutanen suke ta isowa birnin na Karbala mafi yawansu suna tattaki daga birnin Najaf da ke kimanin kilomita 76 daga birnin Karbala din don halarta taron na Arba'in da ake ci gaba da gudanar da shi a yau din nan Juma'a.
Rahotanni daga Irakin sun ce gwamnatin kasar ta dau tsauraran matakan tsaro a garin Karbala din da kewayensa da kuma dukkanin hanyoyin shigowa garin don kiyaye lafiyar masu ziyarar daga duk wata barazana da za ta iya samun lafiyarsu.
Taron juyayin ranar Arba'in din dai ana gudanar da shi ne a ranar 20 ga watan Safar na kowace shekara, wato kwanaki 40 bayan kisan gillan da aka yi wa Zuriyar Annabi a Karbala din a ranar 10 ga watan Muharram na shekara 61.