Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : Pars Today
Litinin

3 Yuli 2017

12:47:29
840172

An Bukaci A Bawa Kasashen Afrika Karin Karfi A Kwamitin Tsaro Na Majalisar Dinkin Duniya

Mataimakin babban sakataren kungiyar tarayyar Afrika ya bukaci a bawa kasashen Afrika karin karfi a kwamitin tsaro na majalisar dinkin duniya wanda yana daga cikin sauye sauyen da ya kamata a gabatar a cikin tsare-tsaren MDD

Kamfanin dillancin labaran reuters ya nakalto Tomasa Kuwaisi Karti mataimakin babban sakataren kungiyar tarayyar Afrika yana fadar haka a jiya Lahadi, ya kuma kara da cewa wannan batun yana daga cikin batutuwan da shuwagabannin kasashen AU zasu tattauna a taronsu na 29 da zasu fara a yau litinin a birnin Addis -Ababa cibiyar kungiyar ta AU. 

Tomas ya kara da cewa tsarin kwamitin tsaro a halin yanzu na yanayin duniya bayan yakin duniya na biyu ne, ya kuma kara da cewa a halin yanzu duniya ta canza, don haka ya kamata a gabatar da sauye -sauye a cikin majalisar daga cikin akwai butar a bawa kasashen Afrika kujerun din-din-din guda biyu sannan wasu karin kujeru 5 na wucin gadi a kwamitin tsaro.

A shekara ta 2005 ma kasashen Afrila sun bukaci a gabatar da sauye sauyye a tsarin tafiyar da majalisar dinkin duniya don ya tafi dai dai da sauye sauyen da aka sami a duniya tun bayan yakin duniya na biyu.