Akwai al'ummar musulmi mazauna Nairobi na kasar Kenya watau "Mahdi Muslim Community" wadanda suka gabatar da yin tir din su da Allah waddai a rubuce dauke da sa hannun shugaban kungiyar Abdulkadi A Nasser.
Haka nan kuma malamai da masana daga ciki da wajen Nigeria suma sun ci gaba da fitar da bayanai kan wannan mummunan ta'addanci na jami'an tsaron Nigeria akan masu tattakin na lumana daga yankin Kano.
Kamar yadda aka sani har yanzun adadin shahidai na wannan waki'ah nata karuwa saboda wadanda a jima raunuka masu muni da harsasai masu rai na jami'an tsaron.
Wata majiya ta tabbatar da cewa ya zuwa yanzun an tabbatar da shahadar sama da mutane 100.