Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : HAIDAR CENTER ACADEMY
Litinin

31 Oktoba 2016

16:54:21
788987

ALAKAR IYAYE DA ‘YA’YANSU

BAHASIN: KARO NA 3 Na Dr, Hafiz Muhammad Sa'id

Addu’a Domin Fata Nagari Ga Yara

Daya daga cikin muhimman abubuwan da

suka hau kan iya ye shi ne; kiyaye yalwa, da

rabautar yaro a cikin rayuwa, wannan kuwa

yana iya kansancewa ta hanyar yi musu

kyakkyawan fata kodayaushe, da kuma yi

musu addu’a mai kyau, kuma tana daya daga

cikin hanyar arzutarsu ta duniya da lahira.

Sannan kuma mu sani cewa; addu’ar iyaye ga

‘ya’yansu tana daga cikin addu’ar da ba a

mayar da ita.

Don haka ne ma gidan da uwaye suke

tsinewa ‘ya’yansu to tabbas wannan gida

yana tare da lalacewa da tabewa, da kuma

talaucewa da daidaicewa, kuma musifar hakan

ba tana takaituwa, ko tsayuwa kan ‘ya’ya ba

ne kawai, tana shafar har su ma iyaye da suka

yi, don haka ne ma yana daga cikin abu mafi

muni iyaye su rika mummunan fata da

muguwar addu’a kan ‘ya’ya, idan suka yi fushi

da su kada su ce komai idan dai ba zasu fadi

alheri ba, idan kuwa zasu fada; to su ce: Allah

ka shirya mana su.

Don haka ne iyaye ku zage damtse wajen yi

wa ‘ya’yanku addu’a ta gari dare da rana,

  • kuma ku ba wa wannan al’amari muhimmanci

na musamman.

Lalacewar mafi yawancin ‘ya’ya sakamakon

mugun baki da la’ana da mummunar addu’ar

iyaye ne, kuma wannan yana shafar har su

iyayen ne, kuma sannan sai ya dame su a

Muna iya ganin wani mutum da ya kai kukan

‘ya’yansa masu tsananin saba masa wajen

manzon rahama (s.a.w), sai Annabi (s.a.w) ya

tambaye shi cewa; Shin ka kyamace su ne (da

mugun baki)? sai ya ce: Haka ne. sai Annabi

(s.a.w) ya ce: Kai ne ka jawo tabewarsu. A

wata ruwayar manzon rahama (s.a.w) yana

cewa: “Ku kiyayi mummunar addu’ar iyaye,

domin tafi takobi kaifi”

Don haka iyaye sai a kiyaye, kuma koda kuna

da hakki kan ‘ya’ya bisa abin da suka saba

muku sai ku kiyaye, balle cewa ma wani lokaci

‘ya’yan ne suke da hakki amma sai iyaye su

runtse idanuwansu, su kawar da kai daga

gaskiya, su yi musu mugun baki!

 Mustadarakul wasa'il, Mirza Nuri, j 5, shafi: 256