#A saki Sheikh Ibraheem Yaqoub El-Zakzaky da gaggawa tare da dukkanin wadanda ake tsare da su a gidajen kaso daban daban.
Masu gangamin sun rika daga tutocin kasar Bahrain da hotunan masu gwagwarmayar Neman hakki da kuma hotunan Sheikh El-Zakzaky suna kira a gaggauta sakin sa tare da dukkanin wadanda suke tsare.
Tun bayan hare-haren ta'addancin da sojojin Nigeria suka kaiwa Harkar Musulunci a Nigeria, da kutsen da suka yi a gidan jagoran Harkar a Gyallesu ake ta gabatar da gangami da muzaharori a baki dayan kasar ana kiran a gaggauta sakin Sheikh El-Zakzaky.
Ga wasu hotunan gaggawa da muka dauka a lokacin gangamin da aka gabatar a yau a babban masallacin Fagge dake kano:288