Bayanin hakan na kunshe ne a wata sanarwa da gwamnatin ta fitar.
Mista Ali ya zama cikakken lauya ne a shekarar 1983, kuma ya zama babban lauyan Najeriya, wato SAN, a shekarar 1997.
A makon da ya gabata ne dai gwamnatin ta Jihar Kaduna ta sanar da mambobin hukumar a karkashin shugabancin Mai Shari'a Mohammed Lawal Garba, shugaban Shiyyar Fatakwal ta Kotun Daukaka Kara.
A watan Disamba ne sojojin Nageria suka afkawa al’ummar musulmi a birnin Zaria, inda mutane da dama suka rasa rayukansu, aka kuma rushe cibiyar 'yan uwa wacce ake kira Hussainiyya da gidan shugaban harkar dake gyallesu wanda a yanzu yake hannun hukumomi, Shaikh Ibrahim Al-Zakzaky.
Sanarwar ta kuma bayyana cewa ranar Juma'a 29 ga watan Janairu za a kaddamar da hukumar, wacce ake sa ran za ta mika rahoton bincikenta makwanni shida bayan ta fara zama.288