Har ya zuwa yau din nan kimanin kwanaki 40 tun daga soma wannan hare-haren ba'a san inda da yawa daga cikin 'yan uwa suke ba. Kamar yadda kuma har ya zuwa yau din nan ba'a baiwa iyalai da dangi gawawwakin wadanda aka kashe ba, don yi musu sutura kamar yadda shari'ah ta tanaza.
Farfesa Dahiru Yahaya na cikin tawagar data sami ganawa da Malam a jiya Laraba 13 ga watan Janairu, 2016 karkashin lemar kungiyar NSCIA kuma bayan ganawar ya bayyanawa 'yan uwa halin da ya ga Malam.
A wata hira da yayi da tashar talbijin ta Al-Wilayah Farfesa ya tabbatar da wannan ziyarar sannan ya ce zasu ci gaba da kokarin ganin an ci gaba da yin irin ta.
'Yan uwa dai na ci gaba da kira a gaggauta sakin Malam ba tare da wani sharadi ba. Haka nan dukkanin sauran 'yan uwa dake tsare a gidajen kaso daban daban, tare da bada gawawwakin wadanda aka kashe don ayi musu sutura.288