Sako mana jagora maulan mu Sheikh Ibraheem Yaqoub El-Zakzaky.
Dukkanin wadan nan gangami ci gaba ne da jerin muzaharori da ake gabatarwa a dukkanin fadin kasar da kasashen waje na yin tir da Allah waddai kan hare-haren ta'addanci na sojojin Nigeria akan Harkar Musulunci da kuma kutsen da suka yi zuwa gidan Sheikh El-Zakzaky wanda ya sabbaba shahadar dimbin mutane da kuma jikkita da dama.
Kamar yadda aka sani ne bayan hare-haren ta'addancin na sojoji sun kuma rika bin gine ginen Harkar da suka hada da makabarta, Husainiya da masallaci suna rugurguzawa.
A Kaduna bayan kammala gangamin 'yan uwa matan sun gana da manema labarai.288