Hare-haren sojoji a Zariya, mika gawawwaki don ayi musu sutura kamar yadda addinin musulunci ya tanada, sakin dukkanin wadanda aka kama aka tsare a gidajen kaso, da sauran su.
Wannan kwamitin dai kamar yadda rahoton ya nuna yayi zaman sa ne a jiya Laraba.
Tuni dai jaridu da mujallu sun fara daukan labarin a fadin kasar Nigeria.
Kamar yadda kowa ya sani dai har yanzun jagoran Harkar Musulunci a Nigeria Sheikh Ibraheem Yaqoub El-Zakzaky yana tsare a hannun hukuma, duk kuwa da irin raunin da ya samu sakamakon kutsen da sojoji suka yi a gidan sa a lokacin hare-haren.288