A wani rahoto da kungiyar ta fitar ta ce shaidun da ta tattauna da su sun gaya mata cewa sojoji sun kashe 'yan Shia fiye da 300 a kwanakin biyu da suka kwashe suna yi musu luguden wuta.
Human Rights Watch ta ce , "Mun tattauna da shaidu 16 da kuma wasu biyar -- cikinsu har da shugabanni -- wadanda suka gaya mana cewa sojojin Najeriya sun yi ta harbin kan mai-uwa-da-wabi a cibiyoyi uku na 'yan Shi'a a Zaria daga ranar 12 zuwa 14 ga watan Disamba. Ba zai yiwu a ce tare hanyar da 'yan kungiyar suka yi ya zama hujjar kashe daruruwan mutane ba".
Kungiyar ta kara da cewa, "Sojoji sun kai hare-hare kan cibiyar Hussainniya Baqiyyatullah, da gidan shugaban 'yan Shi'a, Sheikh Ibrahim Al Zakzaky da gidajen makwabtansa da ke Gyellesu da kuma makabartar 'yan Shi'a, Daral-Rahma, a cikin kwanaki biyu. Shaidu sun gaya mana cewa sojojin sun kashe akalla 'yan Shi'a 300 ko fiye da haka.288