Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : RFI
Alhamis

17 Disamba 2015

14:24:54
725469

CAN da NSCIA na so a yi bincike kan rikicin Shi'a

Kungiyar Kiristocin Najeriya CAN da majalisar koli da ke kula da sha’anin addinin Islama ta kasar, NSCIA sun bukaci gwamnati da ta gudanar da bincike game da kashe mabiya Shi’a a rikicin da ya barke tsakaninsu da sojoji a garin Zaria da ke jihar Kaduna.

A ranar asabar din da ta gabata ne sojojin Najeriya suka yi arangama da ‘yan Shi’a kuma har yanzu an gaza gano hakikanin adadin mutanen da suka rasa rayukansu a tarzomar.

CAN da NSCIA su ne manyan kungiyoyin addini a Najeriya wadanda ke sa ido kan al-amuran da suka shafi Musulmai da Kirista.

CAN ta bukaci shugaba Muhammadu Buhari da ya shiga cikin lamarin tare da gudanar da bincike game da kisan yayin da NSCIA ta kafa kwamitin mutane bakwai domin gana wa da bangarorin da ke rikici da juna, a wani mataki na tabbatar da tsaro da zaman lafiya a Najeriya.288