Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : Harkar musulunci a Nigeria
Laraba

16 Disamba 2015

03:33:41
725151

Anyi gangami a gaban ofishin jakadancin Nigeria dake Tehran

Dimbin al'ummar kasar Iran ne suka yi wani gangami a gaban ofishin jakadancin Nigeria dake birnin Tehran a Jamhuriyar Musulunci Ta Iran, saboda su nuna damuwar su da jajantawa kan mummunan kisan da sojojin Nigeria ta yiwa al'ummar musulmi 'yan uwa na Harkar Musulunci da kuma yin kutse a gidan Sheikh El-Zakzaky

Tare da kona wani bangare na gidan da kuma harbin sa da harsasai da iyalan gidan sa.

Mahalarta gangamin sun rika daga kyallaye dauke da hotuna da kuma rubuce rubuce na abin da ya faru a Zariya.

Haka nan kuma sun rika rera take na Neman a gwamnati da tayi gaggawan dakatar da wannan mummunan aika-aika.288