Ayatullah Akhtari yayi wannan kakkausan suka ne a wata hira da yayi da gidan Talbijin an Al-Alam Iran, yana mai cewa kai hari akan Husainiyar Baqiyyatullah da kuma gidan Malam a unguwar da yake zaune abin tir ne da Allah waddai.
Ayatullah Akhtari tare da bayyana bakin ciki kan abin da ya faru ya yi kira ga sauran al'ummar duniya da su nuna damuwar su, da kuma goyon bayan al'ummar musulmi da aka zalunta a garin na zariya.288