Kamfanin dillancin labaran kasa da kasa na Ahlul-Baiti (A.S) – ABNA – ya habarta cewa: 'yan ta'addar takfiriyya sun
bude wuta kan masallacin Juma’ah da dadadden hubbaren Imam na sharifai a garin
Shah Faisal a birnin Karachi.
A sanadiyar wannan ta'addancin mutane biyu sun jikkata, daya daga cikinsu ma'aikacin masallacin ne.
Lamarin da ya faru na ta'addanci a garin Shah Faisal ya haifar da damuwa ga mazauna wannan yanki.
Bayan sun idar da Sallar Juma'a a gaban hubbaren Imam da wannan ta'addancin ya faru, mazauna garin Shah Faisal sun gudanar da zanga-zangar neman a kama wadanda suka