Kamfanin dillancin labaran shafin sadarwa na Ahlul Bayt (AS) na - ABNA - ya habarta maku cewa: Mintuna Kaɗan Da Suka Gabata; A Daidai Lokacin Da Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Isa Husainiyar Imam Khumaini Domin Halartar Zaɓen Majalisar Musulunci Da majalisar Kwararrun Jagoranci.
A safiyar yau Juma'a 1 ga watan Maris 2024 wanda yayi daidai da 11 ga watan Isfand na shekara ta 1402 Ayatullah Khamenei ya kada kuri'arsa a cikin mintuna na farko na fara kada kuri'ar zaben majalisar dokokin Musulunci karo na 12 da kuma kuri'ar wa'adi na shida na majalisar kwararrun shugabanni a Husainiyyahar Imam Khumaini (RA).