Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : ابنا
Lahadi

4 Faburairu 2024

07:43:26
1435030

Bidiyo Yadda Isra'ilawa Ke Satar tumakin Falasdinawa

Bidiyo Yadda Isra'ilawa Ke Satar tumakin Falasdinawa

Kamfanin Dillancin Labarai na AhlulBait (ABNA) ya habarta cewa: matsugunan da sojojin haramtacciyar kasar Isra'ila ke ba su kariya, sun kai hari a wata rumfar raguna ta Falasdinawa a yankin Arab al-Malihat da ke arewacin birnin Jericho tare da sace wasu daga cikin dabbobinsu. Kamfanin dillancin labaran tashar Aljazeera ya fitar tare da buga hotunan wasu yahudawan sahyuniya wadanda suka kai farmaki a kauyen Ras al-Awja dake arewacin birnin Jericho da ke gabar yammacin kogin Jordan da karfin tsiya tare da goyon bayan sojojin yahudawan sahyuniya inda suka sace tare da kwace wasu tumaki daga hannun Falasdinawa