Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : ابنا
Lahadi

4 Faburairu 2024

07:09:22
1435018

An Rufe Masallacin Sayyidah Zainab As Dake Birnin Alkahira Na Wani Dan Lokaci

Ministan Awkafa na Masar ya ce an rufe masallacin Sayyida Zainab As da ke birnin Alkahira na wani dan lokaci domin a gaggauta aikin gyara da sabunta shi.

Kamfanin Dillancin Labarai na AhlulBait (ABNA): Ministan Awkaf na Masar ya ce an rufe Masallacin Sayyida Zainab As da ke birnin Alkahira na wani dan lokaci domin a gaggauta aikin gyara da sabunta shi.

Muhammed Mukhtar Gomaa ya fada a wani sakon da ya wallafa a shafin X, wanda a da ake kira Twitter, cewa aikin gyare-gyaren yana kan mataki na karshe.

Ya ce rufe masallacin na wucin gadi ya zama dole domin dan kwangilar ya gaggauta gudanar da gyare-gyaren karshe.

An rufe masallacin ne a ranar Alhamis 1 ga watan Fabrairu, kuma ana sa ran bude masallacin kafin a shiga watan Ramadan mai alfarma, in ji shi.

Masallacin Sayyida Zainab As wani masallaci ne mai cike da tarihi a babban birnin kasar Masar. Ya kasance daya daga cikin manya-manyan masallatai kuma mafi girma a tarihin kasar. Kamar yadda wasu bayanai suka nuna, masallacin anan wurin aka binne Sayyida Zainab (SA).

Ya kasance babban wurin gudanar da ayyukan kur'ani da addini a cikin birnin tsawon shekaru aru-aru. Ma'aikatar Awkaf ta aiwatar da aikin gyara na karshe a masallacin a shekarar 1969.