Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : ابنا
Asabar

3 Faburairu 2024

10:09:30
1434755

Mazauna Gaza Da Suka Fake A Iyakar Rafah Suna Cikin Damuwar Hare-Haren Isra’ila

A cikin watanni hudu da suka gabata, Rafah ta fuskanci dimbin Falasdinawa kuma mutane na kwana a cikin tantuna, matsugunan wucin gadi, makarantu da masallatai.

Kamfanin dillancin labaran Ahlul-Baiti (a.s) - ABNA ya habarta cewa: A farkon yakin da yahudawan sahyoniyawan suke yi da kungiyar Hamas, sojojin gwamnatin yahudawan sahyoniya sun ayyana Rafah a matsayin wani yanki mai tsaro, amma a karshe dai ta sha fuskantar hare-hare ta sama daga wannan gwamnati.

Daya daga cikin Falasdinawa mazauna wannan yanki ya ce: Mun zo Rafah ne kamar yadda Isra'ilawa suka ce. Sun ce wannan yanki yana da lafiya da aminci. Amma yanzu an sake yi mana barazana.

Wani Bafalasdine da ke zaune a Rafah ya ce: Mun dauka cewa Rafah ita ce mafakarmu ta karshe. Amma kuma sojojin za su shiga Rafah kamar yadda suka kai hari a wasu sassan Gaza. Babu wani wuri mai aminci a nan.