Kamfanin dillancin labaran shafin sadarwa na Ahlul Bayt (AS) na - ABNA - ya habarta maku cewa: an gudanar da taron tunawa da shahidai na Gaza a yau Litinin 15 ga watan Disamba 2024 a birnin Tehran a karkashin jagorancin kamfanin dillancin labarai na ABNA.
An gudanar da jawaban wannan taron kaitsaye da kuma yanar gizo daga Ayatullah Reza Ramezani, babban sakataren majalisar Ahlul-Bait (AS) ta Duniya da ministan yada labaran kasar Yemen Daifullah Al Shami da wasu manyan mutane daga cikin kasashen Palastinu, Yemen, Iraki, Turkiyya. , da Indonesiya, tare da kasancewar masu kula da kafofin watsa labarai na duniya da masu fafutuka.
A karshen wannan taro an kaddamar da wata fosta na musamman na tunawa da shahidan 'yan jarida fiye da 115 na Gaza.