Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : ابنا
Litinin

15 Janairu 2024

11:15:11
1429497

An Fara Taron Tunawa Da Shahidan 'Yan Jaridun Gaza A Birnin Tehran

An Fara Taron Tunawa Da "Shahidan Gaza" A Tehran 'Yan Mintoci Kadan Da Suka Gabata - Litinin 15 Ga Janairu, 2014 - A Dakin Taro Na Majalisar Ahlul-Baiti (AS) Duniya Tare Da Halartar Babban Sakataren Majalisar Ahlul-Baiti Ta Duniya.

Kamfanin dillancin labaran shafin sadarwa na Ahlul Bayt (AS) na - ABNA - ya habarta maku cewa: an fara gudanar da taron tunawa da shahidai yan jaridu na  Gaza a cikin ‘yan mintoci kadan da suka gabata - a yau ranar litinin 15 ga watan Janairun shekara ta 2024 - karkashin jagorancin Majalisar Ahlul-Baiti. -Bait (A.S) da Kamfanin Dillancin Labarai na Abna.

An fara gudanar da wannan taro ne da jawabai kai tsaye da kuma bidiyo daga Ayatullah Reza Ramezani, babban sakataren majalisar dduniya ta Ahlul-Bait (AS) da kuma ministan yada labaran kasar Yemen da sauran mutane daga kasashen Palastinu, Yemen, Iraki, Turkiyya da Indonesia da tare da halartar manajoji da masu fafutuka a kafafen yada labarai na duniya.