Kamfanin dillancin labaran shafin sadarwa na Ahlul Bayt (AS) na - ABNA - ya habarta maku cewa: Sayyid Hasan Nasrallah acikin bayanansa da ya gabatar ya ce: Sojojin sun gudanar da ayyukan soji sama da 670 a cikin watanni 3 kuma an kai hare-hare a wuraren kan iyaka 48 fiye da sau daya.
Sannan Sayyid Hassan Nasrallah yace: Zamu Ɗauki Fansar Shahadar Al-Aroori Da Shahidan Kerman.
Zamu dauki fansar Al-Aroori Idan muka yi shiru, Lebanon za ta zama mara tsaro.
Ina jaddada cewa har abada jinin shahidan Kerman ba zai tafi a kawai ba.
Har zuwa yanzu muna da damar mayar da yankunan Lebanon da Isra'ila ta mamaye.