Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : ابنا
Lahadi

19 Nuwamba 2023

19:43:58
1413267

Sojojin Yemen: Za Mu Kai Hari Kan Dukkan Jiragen Ruwan Ɗauke Da Tutar Isra'ila

Majiya mai tushe daga Yemen ta jaddada cewa a halin yanzu ma'aikatan jirgin da fasinjansa suna ci gaba da bincike kuma hukumomin Yemen din sun bayyana asalinsu.

Birgediya Janar Yahya Saree, kakakin rundunar sojin Yaman: Bisa la'akari da nauyin da ya rataya a wuyan addini, na kasa da na kyawawan dabi'u da kuma la'akari da irin abin da yankin Gaza ya fuskanta sakamakon wuce gona da iri na gwamnatin sahyoniyawa da Amurka, da kuma yadda suke ta kashe-kashe da kisan kare dangi a kullum, da kuma mayar da martani ga bukatun Al'ummar kasar Yemen da bukatun 'yantattu, domin kai dauki ga al'ummar Gaza da ake zalunta, sojojin kasar Yemen sun sanar da cewa za su kai farmaki kan dukkanin jiragen ruwa da ke dauke da tutar Isra'ila da kamfanonin Isra'ila ke sarrafawa ko kuma mallakar wasu kamfanoni na Isra'ila.

Kamfanin dillancin labaran shafin sadarwa na Ahlul Bayt (AS) na - ABNA - ya habarta maku cewa: Dakarun kasar Yemen sun bukaci dukkan kasashen duniya da su fitar da 'yan kasarsu da ke aiki a matsayin ma'aikatan wadannan jiragen ruwa, da su guji loda kaya aka wadannan jiragen ko kuma su ba su hadin kai, sannan su sanar da jiragensu da su nisanci wadannan jiragen.

Kamar yadda tashar Al-Mayadeen ta fitar cewa: Jirgin ruwan da kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen ta kama yana da ma'aikata 52.

Kasar Yemen ta dakatar da wani jirgin ruwan Isra'ila a tekun Bahar Rum

Al-Mayadeen ta fitar da cewa, sojojin ruwan kasar Yemen sun yi nasarar kwace wani jirgin ruwan sahyoniyawan da ke cikin tekun Bahar Maliya.

Al-Mayadeen ya bayar da rahoton cewa, an kama mutane 52 a cikin jirgin na Isra'ila.

Majiya mai tushe daga Yemen ta jaddada cewa a halin yanzu ma'aikatan jirgin da fasinjansa suna ci gaba da bincike kuma hukumomin Yemen din sun bayyana asalinsu.

Shafin yanar gizo na Axios ya nakalto majiyar yahudawan sahyoniya ya kuma rubuta cewa: Alhuthi (Ansarullah) sun kai hari tare da kwace wani jirgin ruwa wanda wani bangare na wani kamfanin Isra'ila ne.

Kakakin rundunar sojin Isra'ila ya tabbatar da jirgin da aka yi garkuwa da shi, Kame wannan jirgin dakon kaya da 'yan Houthi suka yi a kusa da kasar Yemen a kudancin tekun Bahar Maliya lamari ne mai matukar girma a matakin duniya.

A cewar kakakin rundunar sojin Isra'ila, wannan jirgin da ke kan hanyarsa ta zuwa Indiya daga Turkiyya yana da ma'aikatan da ba na Isra'ila ba.

Alakar Isra'ila da jirgin ba kai tsaye ba ne - an yi hayarsa daga wani kamfanin Burtaniya zuwa wani kamfanin Japan, wanda wani bangare na dan kasuwan Isra'ila Rami Ongar ne.

Ofishin Netanyahu tare da iƙirari na ban dariya da kuma ƙarar zarge-zargen da ake yi wa Iran: Muna Allah wadai da ayyukan Ansarullah, waɗanda ake aiwatar da su tare da jagorancin Iran.

Jirgin da aka kama na wani Bature ne kuma ba ruwansa da Isra'ila!

Muna ba Iran gargadi mai mahimmanci game da abubuwan da suka faru.

Inda kungiyar Ansarullah ta Yaman ta fitar da martani a hukumance kan kame jirgin Isra'ila

Kakakin kungiyar Ansarullah ta Yaman: Mun gudanar da wani sumame na soji a tekun Bahar Maliya inda muka kame wani jirgin Isra'ila tare da ma'aikatansa.

Za mu ci gaba da kai farmakin soji kan makiya yahudawan sahyoniya har zuwa karshen mamayar Gaza.

Kamfanin dillancin labarai na Associated Press: 'Yan kasar Yemen sun kwace jirgin "Shugaban Galaxy" ta jirgin sama mai saukar ungulu da dakarunsu suka sauke su a kan tudu.

Inda kungiyar Jihadin Islama ta Palastinu tafitar da sanarwar jinjinawa ga sojojin Yaman kan wannan gagarumin aiki.

Kungiyar Jihadin Islama ta Palastinu ta yaba da kokarin da sojojin Yamen suke yi na goyon bayan gwagwarmayar Palastinawa a wani gagarumin farmaki da suka kai kan muradun makiya yahudawan sahyoniya, wanda na baya-bayan nan shi ne kame wani jirgin ruwan dakon kaya da ke tafiya zuwa ga gwamnatin sahyoniyawa da kuma kama fasinjojinshi.