Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : ايرنا
Asabar

11 Nuwamba 2023

08:16:21
1410405

Bin Salman: Dole Ne Dakatar Da Yaƙin Gaza

A wani jawabi da ya yi, yarima mai jiran gado na Saudiyya ya yi kira da a kawo karshen yakin da gwamnatin sahyoniya ta ke yi da fararen hula a zirin Gaza.

Kamfanin dillancin labaran shafin sadarwa na Ahlul Bayt (AS) na - ABNA - ya nakalto maku daga Kamfanin dillancin labaran IRNA ya habarta cewa, shafin yada labarai na kasar Russia Today ya habarta cewa, yarima mai jiran gado na kasar Saudiyya Muhammed bin Salman ya bayyana cewa Yatiman ya yi Allah wadai da keta dokokin kasa da kasa da gwamnatin yahudawan sahyuniya ta yi a zirin Gaza a farkon taron kasashen Saudiyya da Afirka a birnin Riyadh.


Ya ce "dole ne a dakatar da hijirar da Falasdinawa ke yi daga zirin Gaza."


Bin Salman ya kuma yi kira da a kawo karshen yakin zirin Gaza tare da aike da kayan agaji.


Yarima mai jiran gado na Saudiyya ya kara jaddada cewa: Saudiyya da kasashen Afirka duk suna goyon bayan duk wani yunkuri na samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.


A yau Riyadh ta karbi bakuncin taron shugabannin Saudiyya da na Afirka, inda aka tattauna kan manyan tsare-tsare tsakanin bangarorin biyu a fannoni daban-daban.


Kamfanin dillancin labaran Irna ya bayyana cewa, yayin da guguwar ta Al-Aqsa ta shiga kwanaki 35, kakakin ma'aikatar lafiya ta zirin Gaza, yayin da yake ishara da mummunan yanayin da asibitoci da cibiyoyin kiwon lafiya a wannan birni suke ciki, ya sanar da karuwar adadin mutanen da su kai shahada na ma'aikatan jinya na wannan birni zuwa mutane 195.


"Ashraf Al-Qdara" ya sanar da cewa: adadin shahidan ma'aikatan lafiya da jiyya a wannan birni ya kai mutum 195, an lalata motocin daukar marasa lafiya 51 sannan an lalata cibiyoyin kiwon lafiya 120, asibitoci 18 sun samu nakasa, da kuma asibitoci 40 a matakin farko sannan cibiyoyin kuma sun yi kasa a gwiwa.


Da yake jaddada cewa gwamnatin mamaya na Isra'ila na da niyyar kai hari kan tsarin kiwon lafiya, ya bukaci kasashen duniya da su gaggauta shiga tsakani don kare tsarin kiwon lafiya da ma'aikatanta a Falasdinu.


A cewarsa, tawagogin likitocin ba su bar filin ba tsawon kwanaki 35, kuma suna kokarin ceto rayukan mutanen da suka jikkata a harin ta’addancin Isra’ila duk da karancin albarkatun da suke da su, amma su kansu an kai musu hari.


Al-Qadra ya roki al'ummar duniya da dukkanin cibiyoyinta na jin kai da kare hakkin bil'adama da su kare tsarin kiwon lafiya da ma'aikatansu ta yadda za su iya gudanar da ayyukansu ba tare da wata barazana ba.


Kakakin ma'aikatar lafiya ta zirin Gaza ya kuma yi nuni da cewa, kwanaki 5 da suka gabata gwamnatin sahyoniyawan ta kai hari a cibiyar kula da lafiya ta al-Shifa, inda wani yaro ya yi shahada tare da jikkata wasu uku, ya kuma kara da cewa gwamnatin haramtacciyar kasar Isra'ila ta kai hari kan al'ummar musulmi da ke Asibitocin Rantisi da na al-Nasr 'yan kasar 8 ne suka yi shahada sannan kuma jami'an lafiya 140 suka jikkata sakamakon haka. Har ila yau, asibitin Quds bai tsira daga wadannan hare-hare ba kuma an kai masa harin inda mutane hudu suka yi shahada yayin da wasu 16 suka jikkata a wannan harin.