Madogara : ابنا
Talata
17 Oktoba 2023
08:33:04
1401947
Falasdinawa da ke zaune a Gaza, wadanda hare-haren da Isra'ila ta kai ya rutsa da su na ci gaba da lalata ababen more rayuwansu, suna fuskantar matsaloli da dama na samar da ruwan sha. Ana ci gaba da fuskantar matsalar ruwan, saboda babu wutar lantarkin da ake bukata da zata raba ruwa a Gaza. Gidan rediyon sojojin Isra'ila ya sanar da cewa an dauke ruwan sha a kudancin Gaza domin tilastawa Falasdinawa yin hijira daga arewa zuwa kudu.