Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : ابنا
Laraba

4 Oktoba 2023

14:02:50
1397826

Shugaban jami'ar Ahlul-Bait (AS) Ta Kasa Da Kasa Ya Gana Da Mataimakin Shugaban Jami'ar Nairobi.

A wannan ganwara Dr. Jazari ya ce: Dole ne mu samar da fahimtar juna kan al'adu da tunanin kasashen biyu wato Iran da Kenya kafin shiga fagen hulda mai ma'ana.

Kamfanin dillancin labaran shafin sadarwa na Kasa da kasa na Ahlul-Baiti (A.S) - ABNA - ya habarta cewa, a gefen guda cikin ziyararsa zuwa Afirka, Dr. Saeed Jazari Mamoui, shugaban jami'ar Ahlul Baiti International ya gana da Farfesa J. Julius Ogeng, mataimakin shugaban jami'ar Nairobi a birnin Nairobi. babban birnin kasar Kenya.

A Cikin wannan ganawar, ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Abna cewa: Jami'ar Nairobi na daya daga cikin manyan jami'o'i a Afirka, kuma tana da matsayi na musamman saboda alakarta da jami'o'i daban-daban na duniya a Turai, Asiya, Gabas da Afirka ta Kudu maso Yamma.

Jazari ya jaddada huldar da ke tsakanin jami'o'in biyu inda ya ce: Jami'ar Nairobi na da kima ga dukkanin jami'o'in kasar Iran saboda nau'o'in darussa daban-daban, da manyan bangarorin karatu tare da kasancewar halartar dalibai daga kasashe daban-daban.

Shugaban jami'ar Ahlul-baiti (AS) ya bayyana cewa: Jami'o'i biyu za su fuskanci matsaloli a fannin musayar dalibai, musanyar malamai da yarjejeniya da fahimtar juna a tsakanin digiri ta hanyar mu'amala da hadin gwiwa, amma ina ganin ya kamata mu dauki matakai. a cikin jagorancin hulɗar ma'amala.

Ya kuma jaddada muhimmancin fahimtar juna ya kara da cewa: Dole ne mu kafa fahimtar juna kan al'adu da tunanin kasashen biyu kafin shiga fagen hulda mai ma'anar data dace. A kasar Kenya, ba a san Iran din Musulunci da al'adunta ba, kuma Iran ba ta da cikakkiyar masaniya kan irin karfin da Kenya ke da shi.

Jazari ya kara da cewa: Dangane da haka, na gana da jami'an jami'ar Nairobi; Matakin farko na wannan mu'amala ya kamata ya kasance ta hanyar fahimtar al'adun Musulunci na Iran da Kenya, wanda ya kamata a fara da jami'an jami'o'in biyu. A mataki na biyu, Jami’ar Ahlul-Baiti ta kasa da kasa (A.S) ta bayyana shirinta na karbar daliban Kenya a matakai daban-daban da kuma samar da damar karatu.

A karshe shugaban jami'ar Ahlulbaiti (AS) ya bayyana cewa: Ba wai mu dage akan ayyukan ilimi da jami'a kawai ba ne, ah ah muna iya yin la'akari da aiki ta fannin gina al'adu da ilimin falsafa.